Kwankwaso Ya Yi Canjin Matsayi, Ya Ba Wa ‘Yan NNPP Ikon Zabe su Je APC

 Kwankwaso Ya Yi Canjin Matsayi, Ya Ba Wa ‘Yan NNPP Ikon Zabe su Je APC

Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano kuma Dan takarar shugaban ƙasa na New Nigeria Peoples Party (NNPP), ya samu cece-kuce a siyasar Najeriya bayan da ya yi sauyin matsayi dangane da batun sauya sheƙa zuwa All Progressives Congress (APC).

A cikin wani ƙanƙanin bidiyo da ya bayyana a kafafen sada zumunta, Kwankwaso ya bayyana cewa ya ba wa duk wanda ke da shirin barin jam’iyyar NNPP ya koma APC ‘damar yin hakan idan suna ganin hakan zai bunƙasa musu damar siyasa. Wannan jawabi ya biyo bayan tsawon jayayya da cece-kuce da aka yi a cikin NNPP akan batun




da shirye-shirye na sauya sheƙa, musamman daga ɓangaren Gwamna Abba Kabir Yusuf na Kano. 

Kwankwaso ya ce cewa yana son a ba wa ‘yan siyasa damar yin amfani da ‘yancin zabe da kai tsaye domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma, maimakon ci gaba da rikice-rikice cikin jam’iyya.

Comments

Popular posts from this blog

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Yi Tattaunawa da Kwankwaso, Daga Bisani Ya Tafi Faransa Don Ganawa da Tinubu

GWAMNATIN TINUBU TA BIYA ‘DAN LOBBYN REPUBLICAN DALA MILIYAN 9 DON LALLABA TRUMP

SHUGABA TINUBU yaki amincewa da sauya shekar gwamnan kano ba tare da kwankwaso ba