Regragui Ya Caccaki Kocin Senegal Kan Janye ’Yan Wasa A Wasan Ƙarshe Na AFCOn
Regragui Ya Caccaki Kocin Senegal Kan Janye ’Yan Wasa A Wasan Ƙarshe Na AFCO N Kocin ƙasar Morocco, Walid Regragui, ya yi kakkausar suka ga takwaransa na Senegal, Pape Thiaw, bayan da ya janye ’yan wasansa daga filin wasa domin nuna rashin amincewa da hukuncin fenariti da alƙalin wasa ya bayar a wasan ƙarshe na gasar AFCON. Lamarin ya faru ne a lokacin da alƙalin wasa ya ba da fenariti da ’yan wasan Senegal suka yi amannar cewa ba daidai ba ne. A sakamakon haka, kocin Senegal ya umarci ’yan wasansa da su fice daga filin wasa a matsayin zanga-zanga, lamarin da ya tayar da kura a duniya kwallon kafa ta Afirka. Da yake martani kan abin da ya faru, Regragui ya bayyana wannan mataki a matsayin “abin kunya”, yana mai cewa hakan bai dace da girman gasar AFCON ba, kuma bai girmama ruhin wasanni da adalci da ake so a kwallon kafa ta Afirka ba. “AFCON babbar gasa ce da ke wakiltar mutuncin Afirka. Abin da ya faru bai kamata ya kasance a irin wannan mataki ba,” in ji Regragui. Ya kara da cew...